Buhari ya sallami shugaban NYSC bayan watanni 6 da naɗa shi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya sallami Shugaban Hukumar kula da Matasa Ƴan yi wa ƙasa Hidima, NYSC, Muhammad Kukah Fadah, ƙasa da watanni 6 da naɗa shi.

Kawo yanzu dai babu wani dalili da a ka bayyana cewa shi ne ya sanya Buhari ya sallami Fadah, amma wata nahiyar sirri a fadar shugaban ƙasa ta shaida wa jaridar PRNigeria cewa korar ta sa ba ta rasa nasaba da rashin ƙoƙari tun bayan da ya kama aiki.
Talla
Sai dai kuma PRNigeria ta jiyo cewa tuni a ka baiwa Fadah umarnin ya mika ragamar aiki ga ma’aikaci mafi matsayi a hukumar wanda zai zama shugaban na riƙo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...