Shirin bunkasa noma da kiwo na kano ya fara gudanar da aiyuka a dajin dansoshiya

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur
Shirin bunkasa noma da kiwo na Jihar Kano, KSADP, ya fara ayyukan gine-gine  da suka kai N2, 509, 343, 144. 10 a wurin kiwo na Dansoshiya da ke karamar hukumar Kiru.
 Shugaban shirin KSADP, Malam Ibrahim Garba ne ya sanar da hakan a lokacin da yake ganawa da masu ruwa da tsaki a Dansoshiya tare da mika wuraren aikin ga ‘yan kwangila.
Wuraren da za’a gina, da nufin mayar da wurin zuwa wurin kiwo na zamani, sun hada da samar da kadada 2,000 na kiwo, da filin kiwo mai fadin hekta 1,000, za’a gina madatsar ruwa, sai gina katanga mai tsawon kilomita 25, da kuma gina titina mai nisan kilomita 20 da samar da na’urorin kashe gobara.
Talla
 Sauran sun hada da gina masallaci da gina rukunin ajujuwa uku, kantin sayar da kayayyaki, gina karamar kasuwa, asibitin dabbobi da kayan aiki, da rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana guda biyar.
 “Muna gudanar da wadannan ayyuka, wadanda za su canza rayuwar makiyaya, domin cika burin gwamnatin jihar kano na samar da tsarin Ruga”, in ji Kodinetan aikin.
 Shirin na Ruga na yunkurin tsugunar da iyalan makiyaya da ke yawo tare da samar da ababen more rayuwa da za su ba su damar jin dadin Inda suke.
 Cikin wata sanarwa da jami’in yada labaran shirin Ameen K Yassar ya aikowa kadaura24, yace Malam Ibrahim Garba ya bayyana cewa baya ga kwangilolin da aka ambata, aikin zai gina tare da samar da a kalla cibiyoyin tattara madara na zamani guda biyar a fadin Dansoshiya a wani bangare na kokarin kara darajar dabbobin su.
 Ya kuma bukaci makiyayan da su ba ‘yan kwangilar hadin gwiwa don ganin an kammala ayyukan cikin gaggawa, yana mai jaddada cewa dole ne ‘yan kwangilar su bi dukanin ka’idojin kwangila na samar da ingantaccen aiki .
 Da yake jawabi a madadin makiyayan, shugabansu, Ardo Abubakar Rabo da sakataren kungiyar ci gaban al’umma ta FULDAN, Muhammadu Majo, sun yi alkawarin bayar da hadin kai sosai don ganin an kammala ayyukan kamar yadda aka tsara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...