Sharri akai min ban jefi Murtala Sule Garo da kofin shayi ba ~ Doguwa

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

A jiya ne dai sa’insa da ka-ce-na-cen ta ɓarke ne lokacin da shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin Najeriya Honorabul Doguwa ya je gidan mataimakin gwamnan Kano a ranar Litinin.

 

Bayan faduwar lamarin magoya bayan Garo sun zargi doguwa da tada hayaniya, wanda Rahotanni ma sunce saida Doguwan ya Jefi Garo da kofin shayi.

 

A zantawar Hon Doguwa da BBC Hausa ya musanya jifan Doguwa ya bayyana cewa ko da ya isa wurin sai ya tarar ana wata ganawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC.

Talla

 

Kuma a cewarsa da ya tambayi abin da yasa ba a gayyace su ba, sai ya ce an mayar masa da kakkausar amsa.

 

“Tambayar kawai da na yi ita ce, ‘yanzu ya mai girma mataimakin gwamna ya kamata a ce ana taro irin wannan, ga ɓangaren gwamnati ga kwamishinoni ga ɓangaren majalisar jiha, amma mu da muke majalisar tarayya ba a gayyaci kowa daga cikinmu ba, laifin me muka yi?

 

“Daga faɗar hakan sai kawai yaron nan Murtala yana zaune ya ce ba za a gayyace ku ɗin ba. Waɗannan kalmomi su suka hassala ni.

 

“A wajen taron kuma a garin yana masifa yana zagina sai ya kifar da wani kofin shayi mai ruwa a ciki, sai santsi ya kwashe shi ya faɗi ya fasa bakinsa.

 

“Amma sai na ji ana ta yaɗa wani zance wan na jefe shi na ji masa rauni,” in ji Doguwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...