2023: Na amince da Atiku a matsayin dan takarar shugaban kasa amma dole Ayu ya sauka –Gwamna Wike 

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 Gwamna Nyesom Wike na jihar Rivers ya sake jaddada kiran cire Iyorchia Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar PDP na kasa.
 Wike ya bayyana cewa ya amince da Atiku Abubakar a matsayin dan takarar shugaban kasa na PDP da kuma Gwamna Ifeanyi Okowa na jihar Ribas a matsayin dan takarar mataimakin Atiku, amma yace dole sai Ayu yayi murabus.
Talla
 Ya yi nuni da cewa murabus din Ayu shi ne kadai hanyar sulhu a jam’iyyar.
 Gwamnan ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ya karbi bakuncin ’yan takarar Gwamna, da Sanata, na Majalisar Wakilai, da na Majalisar Wakilai, da shugabannin Jam’iyyar na kananan hukumomi a gidansa da ke Rumueprikom.
Talla
 Wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai na Wike, Kelvin Ebiri, ya fitar, ta ruwaito shi yana cewa: “Mun kammala zaben fidda gwani na shugaban kasa, shin wike yace a cire dan takarar shugaban kasa? Ko nace a cire dan takarar mataimakin Shugaban Kasa? To, me kuke rokona? Abin da kawai nake cewa, kuma zan ci gaba da cewa, shi ne ba dai dai bane a ka dauki shugaban kasa, da shugaban jam’iyya duk a bangare guda.
Talla
 Ba wanda zai ce nayi gaskiya. Idan na ce a cire dan takarar shugaban kasa, ko idan na ce a cire dan takarar mataimakin shugaban kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...