Rashin ciniki yasa ‘yan kasuwar kofar wambai a kano neman tallafin gwamnatin ta tarayya

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

Kungiyar kasuwar kofar Wambai ta jaddada kudirinta na ci gaba da bijiro da managartan tsare -tsare domin inganta kasuwancin al’ummar kasuwar da bunkasa tattalin arzikin kasuwar da jihar kano baki daya.

Babban sakataren kungiyar kasuwar Alh. Jamilu Yahaya Ibrahim ne ya bayyana haka a lokacin da yake karin haske ga manema labarai dangane da nasarorin da shugabancin kungiyar kasuwar ya samu tun daga farkon kama mulkinsa zuwa yanzu.
Yace kungiyar ta samar da zaman lafiya tsakanin al’ummar dake gudanar da kasuwanci da bakin da suke shiga daga wasu wuraren kasuwar domin yin ciniki da samar da tsaron dukiyoyin yan kasuwar da nemowa yan kasuwa hanyoyin bunkasa jarinsu.
Talla
Sakataren yace, kungiyar ta kuma shigewa ‘yan kasuwa gaba wajen samar musu da rumfuna a kasuwar Dalar Gyada domin ganin sun fadada kasuwancinsu da baiwa wanda bashi da rumfa damar mallakar tasa da shigo da tsarin tallafawa masu karamin karfi da marayu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.
Jamilu Yahaya ya yi kira ga gwamnatin jiha da ta tarayya da su tallafawa kungiyoyin ‘yan kasuwa dake kasar nan duba da yadda kasuwanci yake neman durkushewa a Najeriya, wanda hakan zai haifar da rashin ayyukan yi a fadin kasar nan.
Talla
Haka zalika, ya bukaci al’ummar kasuwar da ci gaba da baiwa kungiyar kasuwar cikakken hadin kai da goyan bayan da ya dace domin ci gaba da bijiro da managartan shire – shiryen da zasu habaka kasuwancinsu a kodaushe, wanda yin Hakan zai Kara farfado da tattalin arzikin jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iya shugabanci: Gwamnan Kano ya sake karbar lambar yabo

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Jaridar Vanguard ta Karrama Gwamnan Jihar...

Kisan Gilla: Muhimman abubuwan da Gwamnatin Kano ta gabatar wa gwamnatin Edo

Hukumomi a jihar Kano, sun yi ƙarin haske game...

Yadda za mu koyawa Matasa 5000 Noman zamani – Shugaban hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are

Daga Rahama Umar Kwaru   Shugaban hukumar raya kogunan Hadeja-Jama'are Engr...

Atiku, El-Rufai, Tambuwal Sun Ziyarci Tsohon Shugaban Kasa – Buhari

Daga Rahama Umar Kwaru   A ranar Juma’a Nan 11 ga...