Dubban ƴan Kwankwasiyya sun tarbi Kwankwaso domin buɗe ofishin NNPP a Kano

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Dubban ƴan Kwankwasiyya ne su ka yi dafifi domin tarbar da kuma gane wa idonsu buɗe ofishin jam’iyyar adawa ta NNPP da ɗan takarar ta na shugabancin ƙasa, Rabi’u Musa Kwankwaso zai yi a jihar Kano a yau Lahadi.

 

Kadaura24 rawaito cewa magoya baya sun dafifi su na tsimayen tsohon gwamnan Kano kuma jagoran NNPP domin buɗe ofishin a unguwar Sharada da ke birnin Kano.

 

Tuni dai gurin ya rincaɓe da magoya baya, babu masakar tsinke, inda hakan ya haifar da cunkoson ababen-hawa a yankin da ma titunan da su kai haɗaka da Sharada.

Talla

A yayin da yake jawabi a wajen taron Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso yace wannan taron ‘yar manuniya ce da abun da zai faru a babban zaben shekara ta 2023.

 

Ya bukaci matasa a ranakun zabe su fito su zabi jam’iyyar NNPP sannan su tsaya domin kare abun da suka zaba domin inganta Rayuwar matasa a jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...