Sabon Kwamishinan kasafi na Kano ya fara aiki

Date:

Daga Kabiru Muhammad Getso

 

A yau ne Sabon Kwamishinan ma’aikatar kasafi da tsare-tsare ta jihar kano Alhaji Ibrahim Dan azumi Gwarzo ya shiga Ofis da domin fara aiki ranar Litinin.

 

Da yake ganawa da manema Labarai Hon Dan Azumi Gwarzo ya bayyana cewa Babban abinda yake bukata ga al’ummar Jihar kano Addu’a domin samun damar sauke nauyin da ya rataya a wuyansa.

 

Yace Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsaren Ma’aikatace da take bukatar bi a sannu tare da sanin makamar aiki, domin bin ka’idojin ayyuka don anfanuwar al’ummar jihar Kano.

Talla

 

Ya Yabawa Gwaman Jihar kano bisa wannan dama da ya bashi ta shugabantar ma’aikatar, inda ya tabbatar da yin aiki tukuru domin anfanin al’ummar jihar kano, musamman ganin yadda yake da kwarewa a fannin.

Talla

 

A shekarun baya dai ya taba rike kwamishinan ma’aikatar kudi kuma ya kammala lafiya ba tare da samun wasu kalubale ba.

 

A makon da yagaba ne Gwamna Ganduje ya Rantsar da sabbin kwamishinoni guda 11 wadanda ya umarcesu da su fara aiki gadan-gadan a wannan rana ta litinin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...