Sabon Kwamishinan kasafi na Kano ya fara aiki

Date:

Daga Kabiru Muhammad Getso

 

A yau ne Sabon Kwamishinan ma’aikatar kasafi da tsare-tsare ta jihar kano Alhaji Ibrahim Dan azumi Gwarzo ya shiga Ofis da domin fara aiki ranar Litinin.

 

Da yake ganawa da manema Labarai Hon Dan Azumi Gwarzo ya bayyana cewa Babban abinda yake bukata ga al’ummar Jihar kano Addu’a domin samun damar sauke nauyin da ya rataya a wuyansa.

 

Yace Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsaren Ma’aikatace da take bukatar bi a sannu tare da sanin makamar aiki, domin bin ka’idojin ayyuka don anfanuwar al’ummar jihar Kano.

Talla

 

Ya Yabawa Gwaman Jihar kano bisa wannan dama da ya bashi ta shugabantar ma’aikatar, inda ya tabbatar da yin aiki tukuru domin anfanin al’ummar jihar kano, musamman ganin yadda yake da kwarewa a fannin.

Talla

 

A shekarun baya dai ya taba rike kwamishinan ma’aikatar kudi kuma ya kammala lafiya ba tare da samun wasu kalubale ba.

 

A makon da yagaba ne Gwamna Ganduje ya Rantsar da sabbin kwamishinoni guda 11 wadanda ya umarcesu da su fara aiki gadan-gadan a wannan rana ta litinin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...