Kano ta yi cikar kwari saboda Auren ‘yar Sarkin Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Birnin Kano ya cika da Baki daga sassa daban daban na ciki da wajen kasar nan domin shaida Daurin Auren ‘yar Sarkin Kano Rukayya Aminu Ado Bayero.

 

Da yake adduar Daurin Auren babban limamin Kano Professor Muhammad Sani Zaharadeen ya ce Ango Amir UK Umar ya biya Sadakin Amaryarsa Rukayya Aminu Bayero naira Dubu Dari biyu.

 

Talla
Talla

Gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ne ya Zama waliyin Rukayya Aminu Ado Bayero, Wanda shi ne ya bayar da Aurenta ga Amir UK Kibiya.

 

Babban sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24 cewa, Sarakuna daga sassan kasarnan da Gwamnoni da manyan Masu kudi da Yan kasuwa na cikin kasar nan da wajenta sun halarci taron Daurin Auren.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Sarki Sanusi Fadi Matsayarsa Kan Hawan Sallah Babba

Daga Sani idris Mai waya   Mai Martaba Sarkin Kano na...

Sallah: Shugaban K/H Rano ya gargadi matasan yankin kan zaman lafiya

Daga Isa Ahmad Getso   Shugaban karamar hukumar Rano Malam Naziru...

Kansila a K/H Garum Mallam ya rabawa marayu 300 kayan Sallah

Daga Safiyanu Dantala Jobawa   Sama da yara mayaru 300 ne...