Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnatin Kano ta ce ta kafa wani kwamiti da zai gaggauta yin nazari da magance yawan ambaliyar ruwa da ruwan sama ke haifar wa a jihar.
Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Muhammad Garba ne ya bayyana hakan a wata sanarwar da ya fitar a jiya Litinin a Kano.
Ya ce gwamnati ta damu da irin ambaliyar ruwan da ke faruwa a jihar, musamman a cikin birni.
Ya ce kwamitin zai ɗauki nauyin duba titina, kwatoci da kwalbati da su ka lalace kuma su ke toshe magudnan ruwa domin a gyara, ko kuma a gina sababbi.
Ya ƙara da cewa kwamitin zai bi duk wasu gine-gine da a ka yi a kan hanyoyin ruwa da su ke haifar da ambaliya domin rushe su.
Kwamishinan ya kuma nuna rashin jin dadin da kuma jajanta wa waɗanda ibtila’in mabakiyar ruwan ya shafa.
Garba ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su kwantar da hankalinsu domin gwamnati za ta tashi tsaye wajen kawo ƙarshen matsalar cikin lokaci kankani.