Ambaliyar ruwa: Gwamnatin Kano za ta rushe gine-gine da a ka yi kan hanyoyin ruwa

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin Kano ta ce ta kafa wani kwamiti da zai gaggauta yin nazari da magance yawan ambaliyar ruwa da ruwan sama ke haifar wa a jihar.

 

Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Muhammad Garba ne ya bayyana hakan a wata sanarwar da ya fitar a jiya Litinin a Kano.

 

Ya ce gwamnati ta damu da irin ambaliyar ruwan da ke faruwa a jihar, musamman a cikin birni.

 

Ya ce kwamitin zai ɗauki nauyin duba titina, kwatoci da kwalbati da su ka lalace kuma su ke toshe magudnan ruwa domin a gyara, ko kuma a gina sababbi.

 

Ya ƙara da cewa kwamitin zai bi duk wasu gine-gine da a ka yi a kan hanyoyin ruwa da su ke haifar da ambaliya domin rushe su.

 

Kwamishinan ya kuma nuna rashin jin dadin da kuma jajanta wa waɗanda ibtila’in mabakiyar ruwan ya shafa.

 

Garba ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su kwantar da hankalinsu domin gwamnati za ta tashi tsaye wajen kawo ƙarshen matsalar cikin lokaci kankani.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...