Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero, ya jajanta wa mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya jajanta wa al’ummar jihar Kano musamman wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a wannan lokaci da ake ta samun ambaliyar ruwa a jihar.

 

A wata sanarwa da mai magana da yawun masarautar Kano, Abubakar Balarabe Kofar Naisa ya sanyawa hannu, Kuma ya aikowa kadaura24, sanarwar tace Sarkin ya bayyana alhininsa game da ambaliyar ruwa da aka gani a wasu sassan jihar.

 

Ambaliyar ruwa: Gwamnatin Kano za ta rushe gine-gine da a ka yi kan hanyoyin ruwa

Sarkin ya yi kira ga al’umma da su guji zubar da shara a hanyoyin ruwa domin kaucewa afkuwar lamarin nan gaba.

 

Yanzu-Yanzu : Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu sakamakon ruftowar wani gini a kasuwar Beruet dake kano

Alhaji Aminu Ado Bayero ya jaddada bukatar malamai su ci gaba da bai wa gwamnati hadin kai domin magance matsalolin ambaliyar ruwa da ta yi sanadiyyar rasa matsuguni da asarar dukiyoyi.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a wurare da daban-daban a jihar Kano an sami ambaliyar ruwa data jawo asarar miliyoyin kudi da Kuma rasa rayuka .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...