Bama So Malam Shekarau da Mutanensa su fice daga NNPP – Abba Gida-gida

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Ɗan takarar gwamnan Kano a jam’iyyar NNPP Engr. Abba Kabir Yusuf wanda aka fi sani da (Abba Gida Gida) ya roƙi Sardaunan Kano Malam Ibrahim Shekarau da mutanensa da suyi haƙuri su zauna a jam’iyyar NNPP don kawar da gwamnatin jam’iyyar APC a Kano.

 

 

Abba Kabir yayi wannan jawabi ne a wani zama da yayi da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar don mayar da martani akan wasu kalamai da Malam Ibrahim Shekarau yayi na zargin rashin adalci da akayi masa a yayin musayar sunayen ƴan takara.

 

“Bama fatan gidan siyasar Shekarau su fita daga jam’iyyar mu, muna fatan zasu fahimci halin da al’ummar Kano ke ciki don ceto su daga wannan hali da suke ciki”. Inji Abba Kabir Yusuf

 

 

Idan dai ba a manta ba, an ja zare tsakanin gidan siyasar Munduɓawa da Kwankwasiyya, inda aka fara yada magana tsakani.

 

jaridar Siyasarmu ta rawaito  anci gaba da raɗe raɗin cewar Malam Ibrahim Shekarau da tawagarsa ƴan shura na iya ficewa daga NNPP zuwa PDP bisa tayin da ɗan takarar shugabancin Kasar nan a jam’iyyar PDP Atiku Abubakar yayi masa na bashi Coodinatansa na shiyyar arewa maso yamma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...