Hukumar Kula da ‘Yan sandan Najeriya za ta tafi yajin aikin sai baba ta gani

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Majalisar hadin guiwa ta Hukumar Kula da ‘Yan sandan Najeriya ta fitar da sanarwar tafiya yajin aikin na sai baba ta gani, saboda saba yarjejeniyar da aka cimma.

 

Shugaban kungiyar ma’aikatan reshen hukumar ‘yan sandan kasar, Adoyi Adoyi, ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da ya yi da jaridar Daily Trust da ake wallafawa a kasar.

 

2023: A shirye muke mu yi kawance da wasu jam’iyyun – NNPP

Kungiyar ta bayyana cewa yajin aikin zai fara aiki ne daga ranar Litinin 29 ga watan Agusta, 2022.

 

Sanarwar na zuwa ne a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin shugaban hukumar Musiliu Smith da babban sufeton ‘yan sandan Najeriya Usman Baba, kan daukar sabbin ma’aikata, musamman karin girma ga kuratan ‘yan sanda.

Gwamnatin Buhari tafi kowacce gwamnati a Nigeria yiwa Kano Aiyukan raya Kasa – Ganduje

 

Shugaban kungiyar ya lura da cewa, babban sufeton ‘yan sandan da sauran shugabannin ‘yan sanda tare da shugaban hukumar, sun yi watsi da dokar daukar sabbin ma’aikata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...