Majalisar dokokin Kano ta amince da sabbin kwamishinonin da Ganduje zai naɗa

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

A yau Litinin ne Majalisar Dokokin Jihar Kano ta tantance tare da amincewa da naɗin kwamishinoni guda tara da gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa.

Tun da fari, hugaban majalisar, Hamisu Ibrahim-Chidari ya sanar da karɓar wasiƙar Ganduje, na neman karin kwamishina ɗaya mai suna Dakta Aminu Ibrahim-Tsanyawa, wanda majalisar za ta tantance tare da tabbatar da shi.

Rundunar yan sanda ta turo sabon Kwamishinan yan sanda jihar kano

 

Idan dai za a iya tunawa, a ranar 15 ga watan Agusta ne kakakin majalisar ya sanar da karbar wasikar da Gwamna Ganduje ya rubuta domin tantancewa tare da tabbatar da wasu daga cikin kwamishinonin da aka nada.

Hakan ya biyo bayan murabus din da wasu ‘yan majalisar zartaswar jihar suka yi na tsayawa takara a babban zaben 2023.

Sabbin kwamishinonin sun hada da: Ibrahim Dan’azumi, Abdulhalim Abdullahi, Lamin Sani-Zawiyya, Ya’u Abdullahi-Yan’shana, Garba Yusuf Abubakar da Dr Yusuf Jibirin.

Mukaman dana rike a gwamnatoci uku yasa nafi kowanne dan takarar gwamna chanchanta a kano – Dr. Gawuna

Sauran sun hada da Adamu Fanda, Saleh Kausami, da Dr Ali Burum-Burum.

Ibrahim-Chidari ya ce an aika da wasikar gayyata ga Ibrahim-Tsanyawa da ya bayyana a gaban majalisar a ranar Talata, domin tantancewa.

An tantance sunayen mutane tara kuma ƴan majalisar sun tattauna kan tantancewar wanda hakan ya sa aka tabbatar da kwamishinonin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...