Musa Iliyasu Kwankwaso na cigaba da daka wawaso a cikin NNPP ta Kura Madobi da Garun Malam

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Dan takarar dan majalisar wakilai a kananan Hukumomin kura, Madobi da Garun Malam a tutar jam’iyyar APC Hon Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso na cigaba da karbar ‘ya ‘yan Jam’iyyar NNPP zuwa APC a yankin.

Hon. Rabi’u Abdulmalik Juda da Alhaji Bala Kubaraci Garkuwa na daga cikin wadanda suka ajiye tafiyar jam’iyyar NNPP kwankwasiyya suka Kuma rungumi tafiyar jam’iyyar APC.

2023: Takarar Sha’aban Sharada nake goyon baya a ADP Kuma zan bashi gudunmawa har ya ci zabe – Rarara

Hon. Bala Kubaraci Garkuwa ya taba zama Mataimaki na Musamman ga Dr Rabiu Musa Kwankwaso Dan Takarar Shugaban Kasa a NNPP Mai kula da jIhar Kaduna, yace lokaci yayi da zasu marawa Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje da Dr Musa Ilyasu baya don samun nasara jam’iyyar APC musamman a yankin Kura Madobi Garun Malam dama Kano baki daya.

Ganduje zai nada matashi mai shekaru 33 kwamishina a kano, waye shi ?

“Ba’a taba mutumin da naso a Siyasance ba kamar Dr Rabi’u Musa Kwankwaso, nayi tallan Kwankwaso da kwankwasiyya a Kano ko Nigeria kadai ba har kasar Ghana naje nayi tallan Kwankwaso, to tunda ka ga bar tafiyar ai kasan akwai dalilai Masu karfi da nake da su”. Inji Bala kubaraci

Da yake zantawa da kadaura24 Dr Musa Ilyasu Kwankwaso wanda shi ne sarkin yakin Masarautar karaye ya yaba da yadda matasan jam’iyyar NNPP suke ajiye tafiyar suna rungumar tafiyar APC.

“Babu Shakka sun yi kyan Kai da suka ajiye tafiyar da ake wahalar da su, suka kuma dawo jam’iyyar APC don su bada tasu gudunmawar don ganin APC ta Sami nasara a zabukan shekara ta 2023”. Inji Musa Iliyasu

Talla
Talla

duk a jiya asabar Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso ya jagoranci guda cikin sabbin yan APC wato Hon Rabi’u Abdulmalik Juda wajen kai ziyara ga dan takarar mataimakin gwamnan kano Hon. Murtala Sule Garo.

Shura ta baiwa Shekarau sharudda 5 na sauya sheka zuwa PDP

Yayin ziyarar sun tattauna muhimman batutuwan da zasu kawowa jam’iyyar APC Nasara a zabukan shekara ta 2023.

Hon. (Dr) Musa Iliyasu Kwankwaso (Sarkin Yakin Karaye) dan takarar majalisar tarayya, shi ne ya jagorancin Tawagar mutanan Kura da garum Malam, wajen kai Wannan ziyara, yan tawagar sun hadar da Hon. Mustapha Abdullahi Kura da Hon.Rabi’u Abdulmalik Juda Sabon dan jam’iyyar APC. da dai sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...