2023: Ban ce zan goyi bayan takarar Tinubu ba – Obasanjo

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya ce ba tattaunawar siyasa suka yi da ɗan takarar shugabanci kasa na APC ba, Bola Ahmed Tinubu.

 

Obasanjo ya gargadi magoya bayan Bola Tinubu kan yaɗa cewa ya marawa takarar Tinubu baya a ganawar sirri da suka yi a gidansa da ke Abeokuta a ranar Laraba.

Musa Iliyasu Kwankwaso na cigaba da daka wawaso a cikin NNPP ta Kura Madobi da Garun Malam

 

Ya ce yaɗa irin wadannan labarai marasa tushe na lahani ga ‘yan siyasa irinsu Tinubu.

 

A wata sanarwa da maitaimaka ma sa na musamman ya fitar, kehinde Akinyemi, na ambato Obasanjo na cewa ganawarsa da Tinubu ta ‘yan uwantaka ce ba siyasa ba.

Ganduje zai nada matashi mai shekaru 33 kwamishina a kano, waye shi ?

Wannan na zuwa ne bayan kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila a wani taro na APC a Lagos ya na mai cewa ganawar Obasanjo da Tinubu alamar nasara ce garesu a zaben 2023.

 

Tsohon shugaba Obasanjo dai ya sake jadada cewa shi uba ne ga duk ‘yan Najeriya da matasa da ke cikin matsi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...