KAROTA ta yi nasarar kama wani matashi mai yin sojan gona da sunanta

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Hukumar dake kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano KAROTA tayi nasarar cafke wani matashi yana sojan-gona da sunan shi Jami’in hukumar KAROTA ne.

 

A cewar mai taimakawa shugaban hukumar kan harkokin kafafen yada labarai na zamani, Ayuba Jarumi, KAROTA ta cafke matashin ne karfe 12 na daren litinin dai-dai lokacin da yake tsaka da tare motoci akan titi yana karbar kudi.

 

Matashin mai suna Lukman Abdullahi mai shekaru 27 mazaunin unguwar Sabon Gari bayan kama shi ya bayyanawa Hukumar Karota cewar shi ɗan Maiduguri ne.

Talla
Talla

Inda ya kara da cewa yana amfani da kayan ne saboda jama’a su fahimci shi ma’aikacin hukumar karota ne.

 

Dama chan Hukumar ta jima tana samun Rahoton yadda matashin yake amfani da sunanta wajen Musgunawa al’ummar Jihar kano, wanda sai a wannan karon dubunsa ta cika.

Rayuwa ta tana cikin Hadari -Hadiza Gabon

Daga karshe shugaban Hukumar ta KAROTA Hon. Dr. Baffa Babba Ɗan’agundi ya shawarci al’umma da su cigaba da kai rahoton duk wani jami’in da suka ga yana karɓar cin-hanci domin ya fuskanci tuhuma.

 

Ya kumace da zarar Hukumar tkammala binke akansa zasu miƙa shi hannun jami’an Yansanda domin faɗaɗa bincike tare da gurfanar da shi a gaban kotu domin fuskantar tuhuma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...