Rayuwa ta tana cikin Hadari -Hadiza Gabon

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

 

Fitaccitar jarumar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon, ta yi ikirarin cewa rayuwarta na cikin hadari saboda yadda ake satar fita da ita daga kotu duk lokacin da aka zauna sauraron shari’arta.

 

Jarumar ta yi wannan bayani ne ta bakin lauyanta, Barista Mubarak Sani Jibril, a gaban wata kotun shari’ar Musulunci a Kaduna.

 

Lauyan na bukatar kotun ta yafe wa jarumar halartar zaman sauraron karar da aka kai ta, tun da tana da wakilci.

 

Talla
Talla

Barista Mubarak ya ce tabarbarewar tsaro ya sa Hadiza Gabon cikin rashin kwaciyar hankali da fargabar abin da ka iya faruwa da rayuwarta idan ta ci gaba da halartar zaman kotun.

 

Radio Nigeria Kaduna ta rawaito lauyan yaci gaba da cewar duk lokacin da Gabon ta halarci zaman kotun, sai dai a yi satar fita da ita.

 

An saki karin fasinjoji biyar na jirgin kasan Abuja-Kaduna

 

“Rayuwata na cikin hadari, rayuwar mai karar ma na cikin hadari. Ba mu san wa ke bibiyar wannan sharia’ar ba a kafofin sada zamunta ba.

 

“Idan ba a yi hankali ba za mu iya ganin mutane dauke da bindigogi domin su sace mu.

 

“Wannan ita ce damuwarmu ba wannan shari’ar ba,” in ji Barista Mubarak Sani Jibril.

 

Gwamna Ganduje ne ya nada umarnin rushe sabon ginin dake gaban gidan Qadiriyya

Lauyan mai kara, Barista Naira Murtala, ya ki yarda da rokon lauyan jarumar, yana mai ikirarin cewa dole ne ta ci gaba da halartar zaman kotu.

 

Alkali Rilwanu Kyaudai, ya tabbatar musu da cewa kotun za ta yi la’akari da lafiyar mai kara da wacce a ke kara a zamanta na gaba.

 

Hadiza Gabon ta halarci zaman kotun ne a ci gaba da sauraron karar da wani ma’aikacin gwamnati mai suna Bala Musa ya kai karar ta a bisa zargin ta ki ta aure shi bayan ya kashe mata kudi Naira 396,000

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...