Rashin tsaro: Sarkin Bichi ya shirya addu’o’in nemawa Nigeria mafita

Date:

Daga Zahraddeen Saleh

 

Dukkanin shirye-shirye sun kammala a majalisar masarautar Bichi domin gudanar da addu’o’i na musamman domin neman taimakon Allah kan matsalar tsaro da sauran kalubalen da kasar ke fuskanta.

 

A wata sanarwa da aka aikowa jaridar kadaura24 mai dauke da sa hannun sakataren masarautar Bichi Alhaji Abubakar Ibrahim Yakasai, ta ce mai martaba Sarkin Bichi Alhaji Nasir Ado Bayero ne zai jagoranci zaman addu’ar a ranar Juma’a 5/8/2022 a babban masallacin juma’a na garin Bichi da karfe tara na safe.

Talla
Talla

Sanarwar ta umurci dukkan malaman limamai da malaman islamiyya da na makarantun allo da ke kananan hukumomi tara na masarautar da su halarci taron.

Sanarwar ta kuma bukaci daukacin al’ummar masarautar da su halarci taron addu’o’in.

Mai Martaba Sarkin Bichi Alh.Nasiru Ado Bayero

Dama dai lokaci zuwa lokaci Mai Martaba Sarkin na Bichi yakan shirya irin wannan taron don yin addu’o’in nema kasa fita dangane da kalubalen matsalar tsaro da sauran matsaloli da kasar take fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...