Rashin tsaro: Sarkin Bichi ya shirya addu’o’in nemawa Nigeria mafita

Date:

Daga Zahraddeen Saleh

 

Dukkanin shirye-shirye sun kammala a majalisar masarautar Bichi domin gudanar da addu’o’i na musamman domin neman taimakon Allah kan matsalar tsaro da sauran kalubalen da kasar ke fuskanta.

 

A wata sanarwa da aka aikowa jaridar kadaura24 mai dauke da sa hannun sakataren masarautar Bichi Alhaji Abubakar Ibrahim Yakasai, ta ce mai martaba Sarkin Bichi Alhaji Nasir Ado Bayero ne zai jagoranci zaman addu’ar a ranar Juma’a 5/8/2022 a babban masallacin juma’a na garin Bichi da karfe tara na safe.

Talla
Talla

Sanarwar ta umurci dukkan malaman limamai da malaman islamiyya da na makarantun allo da ke kananan hukumomi tara na masarautar da su halarci taron.

Sanarwar ta kuma bukaci daukacin al’ummar masarautar da su halarci taron addu’o’in.

Mai Martaba Sarkin Bichi Alh.Nasiru Ado Bayero

Dama dai lokaci zuwa lokaci Mai Martaba Sarkin na Bichi yakan shirya irin wannan taron don yin addu’o’in nema kasa fita dangane da kalubalen matsalar tsaro da sauran matsaloli da kasar take fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...