Ina shan wahala saboda tsadar dizel – Obasanjo

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya yi orafi akan tsadar dizel, da farashin abincin dabbobi da kuma farashin canji da yadda hakan ke shafar noman kifi a Najeriya.

Obasanjo wanda manomin kifi ne ya ce yana cikin tasku saboda tsadar dizel, lamarin da ke kawo tsaiko ga noman kifinsa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Obasanjo ya yi wannan magana ce a jiya Talata a Abeokuta da ke jihar Ogun, a lokacin taron kungiar manoman kifi na yankin kudu maso yammacin Najeria a cikin dakin karatun littafi na Obasanjo (OOPL).

Talla
Talla

Obasanjo ya bayyana cewa cigaba da tashin farashin dizel da kuma cigaba da karuwar farashin abincin kifi zai hana manoman yin aikinsu, sai dai in har sun hada kai su amince da farashi da zasu cigaba da barin su suna sana’ar.

Ya yi bayani yana cewa a halin yanzu farashin dizel 800 ne lita daya, sannan samar da kilo daya na kifi naira 1,400 ne, kuma ya kara da cewa, idan har suna son samun riba, to ba za su iya sayar da kifi kasa da 1500, lamarin da ya su duk wani abu da ya yi kasa da haka zai jawo faduwa ne da asara.

Obasanjo ya ce: “Farashin dizel ya yi sama saboda yadda ake tafiyar da kasar nan ba yadda ya dace ba ne.

‘Ƴan sanda na bincike kan budurwar da ta rataye kanta a Kano

“Saboda haka idan haka ta faru, wasu daga cikin mu da muke bukatar amfani da dizel domin noman kifi zamu yi asarar ne baki daya, kuma a lokacin da hakan zai faru, ‘yan Najeriya za su ci gaba da bukatar cin kifi.”

“Noman kifi zai gagara, sannan manoman da ke wajen Najeriya zasu ringa kawo wa nan.

Rayuwa ta tana cikin Hadari -Hadiza Gabon

“Za ka rasa aikin yi, ka talaue. Saboda haka me ya kamata mu yi? Mu hada kai mu cigaba da raya noman kifi domin kula da bukatun wadanda su ke cin kifi da kuma masu noman kifin,” a cewarsa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...