Shugaban K/H da Kansilolinsa sun fice daga PDP a jihar Sokoto

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban Ƙaramar Hukumar Tangaza ta jihar Sokoto Isah Kalanjine, da kansiloli takwas na majalisarsa sun koma jam’iyyar APC a jihar.

Kansilolin sun hada da Zakariyya Madugu, Abubakar Kalanjine, Abubakar Aliyu, Halilu Aliyu, Ibrahim Tudu da kuma Musa Sakkwai.

Su kuwa Abdullahi Garba da Jamilu Muhammad tsoffin kansiloli ne.

 

Talla

Jaridar The Nation ta rawaito cewa, Jiya ne jagoran jam’iyyar APC, Sanata Aliyu Wamakko da kuma dan takarar gwamna a zaben 2023, Ahmad Sokoto su ka karbi wadanda suka sauya shekar, inda suka ce APC za ta yi nasara a zaben 2023.

Takarar mu da Atiku a PDP babbar barazana ce ga APC – Okowa

Sanata Wamakko ya bada tabbaci ga masu sauya shekar cewa za su ci gaba da tafiya da su wajen ci gaban jam’iyyar da ma jihar baki daya.

Ya kuma tabbatar da cewa APC za ta lashe dukkan kujerun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Likitocin Jinya da Ungozoma sun janye yajin aiki – Ministan lafiya

Ƙungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Ƙasa (NANNM) ta...

Sarkin Hausawan Arewa, Amb. Balarabe Tatari, Ya Aike da Sakon Ta’aziyyar Buhari da Dantata

Sarkin Hausawan Arewa kuma Ambasadan Zaman Lafiya, Alhaji Balarabe...

INEC ta sanya ranar fara rijistar masu zabe a Nigeria

Hukumar zaɓen Najeriya ta ce nan gaba cikin wannan...