Shugaban K/H da Kansilolinsa sun fice daga PDP a jihar Sokoto

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban Ƙaramar Hukumar Tangaza ta jihar Sokoto Isah Kalanjine, da kansiloli takwas na majalisarsa sun koma jam’iyyar APC a jihar.

Kansilolin sun hada da Zakariyya Madugu, Abubakar Kalanjine, Abubakar Aliyu, Halilu Aliyu, Ibrahim Tudu da kuma Musa Sakkwai.

Su kuwa Abdullahi Garba da Jamilu Muhammad tsoffin kansiloli ne.

 

Talla

Jaridar The Nation ta rawaito cewa, Jiya ne jagoran jam’iyyar APC, Sanata Aliyu Wamakko da kuma dan takarar gwamna a zaben 2023, Ahmad Sokoto su ka karbi wadanda suka sauya shekar, inda suka ce APC za ta yi nasara a zaben 2023.

Takarar mu da Atiku a PDP babbar barazana ce ga APC – Okowa

Sanata Wamakko ya bada tabbaci ga masu sauya shekar cewa za su ci gaba da tafiya da su wajen ci gaban jam’iyyar da ma jihar baki daya.

Ya kuma tabbatar da cewa APC za ta lashe dukkan kujerun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...