Kananan sana’o’in da mata ke yi na kara habbaka tattalin arzikin kasa – Maryam Gawuna

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

Shugabancin kungiyar kasuwar Singa ya bukaci Gwamnati ta tallafawa mata da suke gudanar da kasuwancinsu a kasuwar domin habaka kasuwancinsu da ci gaban tattalin arzikin jihar Kano.

 

Shugabar dake kula da al’amuran mata ta kungiyar kasuwar, Hajiya Maryam Musa Gawuna ce ta bukaci haka a wata tattaunawa da manema labarai a kasuwar ta Singa.

Talla

 

Maryam Gawuna ta ce tallafawa mata da jari a kasuwanci yana da mutukar mahimmanci saboda su sun iya ririta kudi ko ya yake, don haka idan aka tallafa hakan zai ingata rayuwar su da Kuma ciyar da tattalin arzikin jihar kano dana kasa gaba.

INEC ta rufe yiwa yan Nigeria rijistar katin zabe

 

Shugabar ta yi kira ga Gwamnatoci a dukkanin matakai, da su ci gaba da tallafawa mata da jari domin rage masu zaman kashe Wando da yawaitar talauci tsakanin al’umma.

 

Hajiya Maryam Gawuna, ta kuma yi kira ga mata da su daina raina kananan sana’o’i duba da cewa daga karamar sana’a ne, ake samun bunkasa ta zamo babba, inda tace yanzu lokaci ya canza an daina raina kananan sana’o’i ana gudanar da sana’o’in ne don rufawa kai asiri.

Shugaban K/H da Kansilolinsa sun fice daga PDP a jihar Sokoto

mata suna da rawar takawa a fannin harkokin kasuwanci da bunkasar tattalin arziki a kasar nan, shi ya sa kamata ya yi Gwamnatocin jihohi dana tarayya su yi duk mai yiyuwa domin ganin sun tallafawa mata da jarin da za su rike kansu da iyalansu”. Inji Maryam Gawuna

 

Daga karshe ta yi kira ga yankasuwa da masu hannu da shuni da su rika saukakawa a kayayyakinsu da zarar, sun samesu a cikin sauki domin al’umma su ji dadin gudanar da rayuwa cikin sauki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...