Ana zargin ‘yan Vigilante da kashe malamin makarantar allo a Jihar Kano

Date:

Daga Umar Ibrahim

 

Ana zargin ‘yan kungiyar sintiri (vigilante) da kashe wani malamin makarantar allo a unguwar Dabai, da ke karamar hukumar Gwale a Jihar Kano.

 

Shi dai Musa Mai-Almajirai, sanannen malamin Qur’ani ne a unguwar, inda yake da daruruwan almajirai.

 

Ana zargin ‘yan kungiyar sintirin da yi wa malamin dukan tsiya a ofishinsu bayan da aka kai shi can bisa zargin da wata mata ta yi masa na yunkurin satar yaro.

Talla

Jaridar Premium Times ta intanet ta ruwaito cewa dan malamin, Ibrahim ya sheda mata cewa, ”Mahaifin nasa yana tafiya ne sai ya ji kukan jariri sabuwar haihuwa a wata bola.

Da dumi-dumi: Gwamna Ganduje da Sarki Sanusi sun yi kicibis a Abuja

Sai ya je ya dauki yaron, sai kawai wata mata ta yi masa ihu, tana ce masa barawon yaro.”

 

”Kururuwar da matar ta yi ce ta janyo ‘yan kungiyar sintirin da sauran jama’ar unguwar wadanda suka rufe shi da duka,” in ji dan.

NDLEA ta rufe gidan abincin da take zargin ana sayar da kayan maye a Kano

 

Ya kara da cewa, ”Daga nan sai suka tafi da shi ofishinsu suka ci gaba da dukansa. Daga baya ya fadi ya suma.”

 

Ya ce,” Bayan da wasu ‘yan unguwar suka gane shi sai suka garzaya da shi asibiti, inda ya cika a hanya.”

 

Dan malamin ya sheda wa jaridar cewa ‘yan-sanda sun kama shugaban ‘yan-sintirin na unguwar, mai suna Munkaila, inda ake bincikensa a caji ofis na Rijiyar Zaki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...