Kungiyar BAT dake goyon bayan Tinubu ta nada Darakta da Sakataren ta a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Babban Daraktan Ƙungiyar APC Media and Mobilization Group for Ahmed Bola Tinubu (ABT) na shiyyar Arewa maso Yamma Amb. Aminu Nuruddeen Amin ya miƙa takardun kama aiki ga Hon. Tijjani Sani Amasko da Hon. Kabiru Aluta Dambatta a matsayin director da Secretary na jihar Kano a madadin shugaban ƙungiyar na ƙasa Comrade Kingsley Omadoye.

 

Amb. Aminu yace bai yi wannan zaɓi da ka ba sai da yayi zuzzurfan bincike sannan ya gano cewa babu wasu jajirtattun matasa a jihar Kano waɗanda suka shahara wajen tallata jam’iyyar APC da ƴan takarkarinta na kowanne mataki kamar Tijjani Sani Amasko da abokan aikin sa.

Wata kotu a Kano ta yanke hukuncin biyan diyya ga wani gani matashi da aka sara a hannu

Ya tabbatar da cewa idan suka karɓi abu to sunayi da gaske, kuma suna da tsayayyen tsarin da duk saƙon da suka karɓo zasu aikashi kuma zai dire har ƙasa kasancewar suna da tsarin da ya taho daga jiha, shiyya zuwa ƙananan hukumomi ya tafi har mazaɓu.

Amb. Aminu Nuruddeen a madadin shugabanninta na ƙasa ya tabbatar da cewa wannan ƙungiya tana biyayya sau da ƙafa ga jigo a tafiyar Tinubu wato Dr. Abdullahi Umar Ganduje OFR, kuma tuni yana cikin iyayen wannan ƙungiya na Arewa Maso Yamma.

A ƙarshe, An bayar da shawarwari tare da addu’ar Allah S.W.T ya bawa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin sa Sen. Kashim Shettima nasara a zaɓen 2023 mai zuwa, Ameen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...