Da dumi-dumi: Tinubu ya zabi tsohon gwamnan Borno a matsayin mataimaki

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Dantakarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Bola Ahmad Tinubu ya sanar da Kashim Shettima tsohon gwamnan jihar Borno a matsayin wanda zai masa mataimaki a zaben 2023 mai zuwa.

 

Tinubu ya sanar da hakan ne yayin tattaunawarsa da manema labarai a jihar Katsina, jim kaɗan bayan ziyarar Sallah da ya kaiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Ku yi amfani da lokacin Sallah Babba don yiwa kasa addu’o’in samun Zaman lafiya – Hon. Nassir Ali Ahmed

“jiga-jigan jam’iyyar APC, an zabi Shettima ne saboda tsohon gwamnan jihar Borno ne kuma yana da  “Kwarewar aiki, kuma mutum ne da kowa zai aminta da shi hakan tasa na zabe shi a matsayin abokin takarata”. Inji Tinubu

 

An jima dai ana kai ruwa rana kan wanda zai zama mataimakin sa a takarar shugaban kasa da yake yiwa jam’iyyar APC.

Kawu Sumaila ya taya al’ummar Musulmi Murnar Sallah Babba, ya bakuci su hada Kai

Idan ba’a manta ba, Kadaura24 ta rawaito ko a ranar juma’ar data gabata sai da gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ce su suka baiwa Tinubun shawarar ya dauki Musulmi a matsayin mataimakin sa duk kuwa da kalubalen da zasu fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...