Daga Ali Kakaki
Shugaban jami’ar Maryam Abacha American University MAAUN dake Najeriya da Niger,farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya bayyana ya cewa burinsa shi ne ilimantar da mutane sama da Miliyan 1 kafin ya bar duniya.
Farfesa Gwarzo ya bayyana Hakanne a wata hira da yayi da kafar yada labarai ta BBC Hausa a ranar Lahadi.
Farfesa Gwarzo yace yana da kyau jami’o’i na gwamnati da masu zaman Kansu, su yi hadin gwiwa wajen kawo ci gaba a fanni ilimi a kasar nan, Wanda burinsa a Kullum shi ne ya kawo sauyi da ci gaba acikin harkar ilimi a Nijeriya da Arewa baki daya.
Kawu Sumaila ya taya al’ummar Musulmi Murnar Sallah Babba
Gwarzo ya ce ,kawo yanzu ya dau nayin karatun ‘yayan talakawa da suke da kwazon karatu a tsarin tallafin karatu wato scholarship a kasar Niger sun Kai mutum Dubu.
Ganduje ya yiwa fursunoni sama da 3,800 afuwa cikin Shekaru 7
A karshe shugaban jami’ar ta MAAUN, ya bukaci gwamnati ta duba matsalolin da jami’o’in gwamnati ke ciki na yajin aiki domin nan ne kadai Dan talaka yake samun damar yin karatu cikin sauki.