Ku yi amfani da lokacin Sallah Babba don yiwa kasa addu’o’in samun Zaman lafiya – Hon. Nassir Ali Ahmed

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Nasarawa a majalisar wakilai ta kasa, Hon. Nassir Ali Ahmed ya taya al’ummar jihar Kano murnar bikin Sallah Babba.

A wata sanarwa da dan majalisar tarayya ya fitar a ranar Lahadin, ya bukaci al’ummar jihar da su yi amfani da lokacin bikin Sallah wajen yin addu’ar samun zaman lafiya a jihar da ma kasa baki daya.

Hon. Nassir Ali Ahmed ya tabbatar wa al’ummar mazabar sa cewa nasarorin da ya samu a wakilcin da yake yi musu ya same su ne bisak jajircewar sa wajen ganin sun samu wakilcin da ya dace a zauren majalisar.

Da dumi-dumi: Tinubu ya amince zai dauki Mataimaki Musulmi a zaben 2023

Ya kuma bukaci al’ummar musulmi da su kiyaye kyawawan dabi’un Musulunci wanda ya ya koya wa mabiyansa ta yadda za su zauna lafiya ba kawai da ‘yan uwa musulmi ba, har ma mabiya sauran addinai.

Hon Nassir Ali Ahmed ya kara da cewa, ba za a iya samun zaman lafiya da hadin kai a Najeriya ba, in ba tare da hakuri a tsakanin mabiya manyan addinai biyu na Musulunci da Kirista ba.

Burina shi ne Ilimantar da mutane miliyan Ɗaya kafin na bar Duniya – Farfesa Gwarzo

Bugu da kari, ya bukaci al’ummar musulmi da su rika nuna kauna da taimakawa ga makwabtansu da sauran jama’a, yayin da suke gudanar da bukukuwa irin wadannan masu muhimmanci a rayuwarsu.

Ahmed ya kuma yi fatan wannan lokaci na Sallah ya zama silar samun albarka, zaman lafiya, wadata da aminci ga ‘yan Nijeriya ganin cewa idan aka yi addu’a a wadannan kwanaki kalubalen da kasar nan ke fuskanta za su zama tarihi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...