Na yi Imani Allah Zai baku ladan Niyyar aikin Hajjin da ku kai – Bn Sina ya fadawa Maniyatan da basu je makka ba

Date:

Daga Haleema Umar Sabaru

 

Shugaban kwamitin bita na hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano Sheikh Harun Muhd Sani Ibn Sina yace maniyatan jihar nan da basu Sami zuwa kasar Mai tsarki su dauka cewa haka Allah ya kaddara musu, kuma akwai kyakyawan yakinin zasu Sami ladan niyyar da sukai.

Kadaura24 ta rawaito Sheikh Harun Ibini Sina ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai a nan Kano.

Shugaban kwamitin bitar wanda shi ne kwamandan Hisbah na jihar Kano yace kamata yayi maniyatan su Mai da lamarin su ga Allah, su dauka cewa haka ya tsara kuma babu wanda ya Isa ya sauya hukunci Allah.

Yace abun da ya faru suma basu ji dadin faruwar sa ba, kuma hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ta yi iya bakin kokarinta don ganin an kwashe dukkanin maniyatan jihar Kano Amma lamarin yaci tura.

Yace yanzu haka Shugaban Hukumar Jin dadin alhazai ta Kano Farfesa Sale Pakistan bai Sami tafiya ba, Sakataren zartarwar hukumar ma haka da dai Sauran daraktocin Hukumar,duk da suna da damar zuwa, amma sun hakura saboda jimamin abun da ya faru ga maniyatan jihar Kano Dana wasu jihohin.

Sheikh bn Sina yace duk da basu je saudiyyan a bana ba, Amma sun gudanar da kyakyawan tsarin yadda za a cigaba da yiwa Mahajjatan Kano bita har a kammala Ibadar aikin Hajjin ta bana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...