Sale Kala Kawo ya zama Zababben Shugaban APC Media Forum a Kano

Date:

Daga Yakubu Abubakar Gwagwarwa

 

Kungiyar APC Media forum, yan jam’iyyar APC masu magana a kafafen yada labarai sun gudanar da zabe a yau talata Inda suka zabi Sale Kala Kawo a matsayin Sabon zababben shugaban kungiyar.

 

 

An gudanar da zaben ne karkashin kulawar jam’in zabe Ahmad Musa wanda shin ya bayyana sakamakon zaben bayan an kammala kada Kuri’u kamar yadda kundin tsarin kungiyar ya tanada .

 

Gwamnatin Katsina ta tabbatar da bullar cutar Kyandar Biri a jihar

Ahmad Musa yace Sale Kala Kawo shi ne ya lashe zaben da Kuri’u guda 76 wanda hakan ta nuna shi ya Sami kuri’a Mafi rijiye kuma ya cika dukkanin ka’idojin zabe don hakan” Na ke tabbatar da cewa Sale Kala Kawo shi ne sabon zababben shugaban wannan kungiyar ta APC Media forum”.

 

 

Chairman Hon Sale kala Kawo

 

Mataimakiyar sa Hannatu Abdulkadir ta

 

Sakataran kungiya Hon Umar Mai Rice

 

Ma’ajin kungiya Shamsu Mai Shadda

 

Shugaban Mata Karimatu Musa Matashiya

 

Sakataran Tsare Tsare Adamu Danjuma Isa

 

Sai kuma Hon. Abdullahi Maikano Zara na daga cikin iyayen kungiya.

 

A zantawarsa da wakilin kadaura24 bayan bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben Sale Kala Kawo ya bukaci sauran ‘ya’yan kungiyar wadanda suke adawa da bangarensu dasu zo su hade don ciyar da kungiyar da jami’ar APCn Kano gaba.

Na yi alkawari shirya sahihin zaben Kungiyar APC Media forum ta Kano – Ibrahim Maishinku

Sale Kala ya godewa duk shugabannin kwamitin da suka shirya zaben bisa dattako da suka nuna, sannan kuma ya yabawa wakilan jami’an tsaro wadanda suka halacci zaben don ganin ya gudana lafiya.

 

Sale Kala Kawo dai ya taba riƙe shugaban kwamitin rikon kungiyar a baya ganin ya sauka har aka shirya zaben da ya bashi Nasara. Inda a gefe guda kuma wasu yan kungiyar nacan suna shirin shirya wani zaben don zabar wasu shugabannin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...