Gwamnatin Katsina ta tabbatar da bullar cutar Kyandar Biri a jihar

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

An samu bullar cutar Kyandar Biri a Katsina kamar yadda gwamnatin jihar ta tabbatar.

 

Gwamnatin ta tabbatar cewa cutar ta harbi mutum daya yayin da ake dakon sakamakon wasu samfura 15 daga dakin gwaje-gwaje da aka kai Abuja, babban birnin kasar nan.

 

Kwamishinan Lafiyar jihar, Yakubu Nuhu Danja ne ya tabbatar da hakan ranar Talata, yayin kaddamar da shirin rarraba magunguna kyauta da kuma cibiyar kiran nema agajin gaggawa a Ofishin Hukumar Lafiya a Matakin Farko na jihar.

 

Mu fito mu Tsaftace Muhallanmu don gujewa ambaliyar ruwan sama – Falakin Shinkafi

 

“Mun tabbatar da cewa cutar kyandar biri ta harbi mutum daya kuma an dauki dukkan matakan da suka dace na yi wa marar lafiya magani da tuni an sallame shi.

 

“Muna da wasu mutum 15 da aka zargin sun kamu da cutar wadanda aka kai samfurin jininsyu dakin gwaje-gwaje da ke Abuja.

 

 

 

“A yanzu haka muna sa ran sakamakon gwaje-gwajen zai fito nan da mako guda,” a cewarsa.

 

Duk da karin lokacin jigila, maniyyatan Najeriya 8,000 za su iya rasa Hajjin bana

 

Daily News24 ta rawaito dangane da aikin rarraba magunguna da gwamnatin jihar ta kaddamar, Kwamishinan ya ce hakan wani mataki na tunkarar yiwuwar barkewar cututtuka da galibi akan samu a irin wannan lokaci na damina.

 

“A yanzu haka mun tanadi rigakafin magance annobar cututtuka irinsu cutar Sankarau, Kyanda da Kwala.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...