Mu fito mu Tsaftace Muhallanmu don gujewa ambaliyar ruwan sama – Falakin Shinkafi

Date:

Daga Sayyadi Abubakar Sadiq

 

Wani Dan kishin kasa kuma Mai rike da sarautar Falakin Shinkafi Ambasadan Zaman lafiya Amb. Yunusa Yusuf Hamza ya hori al’ummar jihar kano dana kasa baki daya da su himmatu wajen yashe magudanan ruwansu don gudun ambaliyar ruwan sama.

 

Yace barin magudanan ruwa ba tare da yashe su ba, musamman a wannan lokaci na damuna yana da hadari sosai saboda shi yake kawo ambaliyar ruwan sama

 

Amb. Yunusa Yusuf Hamza ya bayyana hakan ne yayin wata ganawarsa da wakilin kadaura24 a safiyar talatar nan .

 

Yace ya kamata mutane su daina jiran sai gwamnati ta zo ta yi musu yasar magudanan ruwa a unguwannin su, saboda abubuwa su yiwa mata yawa kuma idan aka tsaya jiranta abun da ba’a fata ya faru.

 

“ku kuke zaune a unguwannin ku kuma idan matsala ta zo ku Zata fara shafa, domin kune zaku yi asarar rayuka da dukiyoyin ku, don haka ku yafi dacewa ku taimakawa kanku don kaucewa waccen matsalar.” inji Falakin Shinkafi

 

Amb. Yunusa Yusuf yace kamata yayi gwamnati da masu ruwa da tsaki a kowacce unguwa su baiwa yashe magudanan ruwa muhimmanci ko a rage afkuwar ambaliyar ruwan sama a Cikin al’umma.

 

kadaura24 ta rawaito Amb. Yunusa Yusuf Hamza ya kan je unguwar su ta Yakasai a duk asabar din karshen wata, domin shiga Cikin matasan da suke aikin yashe magudanan ruwa unguwar don karawa matasan kwarin gwiwar tsaftace yankin nasu

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...