Hadari ya rutsa da jerin gwanon motocin Gwamnan Benue

Date:

Haduran mota da aka samu a sassan Najeriya daban-daban a karshen makon sun yi sanadiyyar mutuwar motum 30 tare da raunata wasu da kuma asarar dukiya.

 

Hukumomin kasar sun danganta haduran da saba ka’idojin hanya da gudun da ya wuce kima da kuma tafiye-tafiyen dare.

 

Jaridar DailyTrust ta kasar ta ruwaito cewa daga cikin haduran, wasu da suka auku a tsakanin ranakun Asabar da Lahadi, sun yi sanadiyyar mutuwar mutum 18 a gadar Isara da ke jihar Ogun, kan tagwayen hanyar Lagos zuwa Badun.

 

Sannan wasu mutum 10 sun rasu a kan titin Potiskum zuwa Gombe a Jihar Yobe, yayin da wasu mutum biyu suka rasu a wani hadarin motar a kan titin Lokoja zuwa Obajana zuwa Kabba.

 

A hadari na hudu, wanda shi kuwa ya rutsa ne da kwambar motocin Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom, a Abuja, rahotanni sun ce motoci hudu wasu tireloli biyu suka murkushe, yayin da wata motar jami’na tsaro a kwambar ta yi karo da wata motar kirar Golf, sai dai ba wanda ya rasa ransa, a hadarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...