Tinubu yace har yanzu yana laluben wanda zai yi masa takarar mataimakin

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu, ya ce har yanzu yana neman wanda zai yi masa mataimaki.

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi a Abuja, a lokacin kaddamar da wani littafi a bikin cika shekara 60 da haihuwar Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila.

Dan takarar yana da dama har zuwa ranar 15 ga watan Yuli kamar yadda hukumar zaben kasar ta tanada ya mika mata sunan wanda zai maye gurbin Kabir Ibrahim Masari, wanda ya bayar da sunansa domin rike wannan mukami na wucin-gadi.

Tinubu, ya yaba wa Kakakin Majalisar Wakilan a kan irin gudummawar da ya ce yana bayarwa ga dumokuradiyya, yana mai cewa abin da ya yi masa a lokacin zaben fitar da gwani abu ne da ba zai iya ambatawa ba a wannan lokaci.

Ya ce, ”Na kashe lokaci mai yawa, lokaci da dama, mutane za su iya kagara, za su iya kyashi, za su iya bakin-ciki ma. Na yi gagarumar nasara, na gode ma.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...