Tinubu yace har yanzu yana laluben wanda zai yi masa takarar mataimakin

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu, ya ce har yanzu yana neman wanda zai yi masa mataimaki.

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi a Abuja, a lokacin kaddamar da wani littafi a bikin cika shekara 60 da haihuwar Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila.

Dan takarar yana da dama har zuwa ranar 15 ga watan Yuli kamar yadda hukumar zaben kasar ta tanada ya mika mata sunan wanda zai maye gurbin Kabir Ibrahim Masari, wanda ya bayar da sunansa domin rike wannan mukami na wucin-gadi.

Tinubu, ya yaba wa Kakakin Majalisar Wakilan a kan irin gudummawar da ya ce yana bayarwa ga dumokuradiyya, yana mai cewa abin da ya yi masa a lokacin zaben fitar da gwani abu ne da ba zai iya ambatawa ba a wannan lokaci.

Ya ce, ”Na kashe lokaci mai yawa, lokaci da dama, mutane za su iya kagara, za su iya kyashi, za su iya bakin-ciki ma. Na yi gagarumar nasara, na gode ma.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...