A Zaman kotun yau, lauyan Abduljabbar ya roki Kotu ta Sallami wanda yake karewa

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

A zaman kotun na yau karkashin jagorancin Mai Sharia Ibrahim Sarki Yola kotun taci gaba da sauraran shari’ar Malam Abduljabbar Sheikh Nasir Kabara.

Inda Lauyan gwamnati Barista Yakubu Abdullahi ya gabatar da kansa tare da mataimakansa, haka kuma lauyan wanda ake kara wato Barista Dalhatu Shehu ya gabatar da kansa nan take, Lauyan gwamnati ta bakin Barista Abdurrahman Muktar yavfara yiwa malamin tambayoyi ciki kuwa hadda cewar wannan kur’anin da muke anfani dashi cikakkene? Malamin yace kwarai kuwa

Sannan Kuma yayi Masa tambayar cewar menene matsayin karatunsa ? anan ne aka dinga Kai Ruwa Rana daga karshe malamin yace yana da digirin digirgir Wanda yasamu daga hadakar wata jami’ar Amurka dake Ghana, haka kuma malamin anyi masa tambayar Ijaza wato kwalin dake tabbatar da sahihancin iliminsa nanma yace akwai na gidansu da kuma wani malami a kasar Morroco.

Kazalika lauyan gwamnati ya yiwa Abduljabbar tambaya akan cewar suna da wata akida ta cewar Alkurani ba cikakke bane? malamin ya musanta hakan, inda yace shi dai y abada bayani daga cikin wasu littatafai.

Bayani kammala tambayoyinne sai Lauyan Wanda ake tuhuma ya tashi yace yana da magana, bayan da Mai shari’a ya Amin ce masa, sai ya roki kotu data sallami malamin, sannan yace bayanan da aka gudanar kan malamin basu ingantaba don haka ya roki kotun ta sallami malamin ta kuma umarci gwamnati tabashi hakuri da kuma Neman afuwa gareshi.

Ta ke Lauyan gwamnati ya yi suka kan bukatar lauyan Abduljabbar din, yace ya fadi haka ne saboda batun lauyan gwamnati ba shi da muhalli a cikin sashi na 390(2) Amma yana da damar kalubalantar cajin kafin hukunci.

Daga karshe dai kotun ta daga sauraren shari’ar har zuwa ranar 7/7/2022 domin fadar ra’ayinta akan yuwuwar sallamar Wanda ake zargi ko Kuma akasin haka.

Wakiliyar kadaura 24 Rukayya Abdullahi Maida ta rawaito mana cewa lauyan gwamnati Barista Lamido Abba Soran dinki yace ai Babu batun sallama tunda sun gama bada bayanin tuhumar yayin zantawarsa da manema labarai.

Anashi bangaren Lauyan dake Kare malam Abduljabbar wato barista Dalhatu Shehu ya kara tabbatar da rokonsu ga kotu na sallamar Malamin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yansanda sun Haramta Hawan Sallah a Kano

Daga Abdulmajid Habib   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta haramta...

Sanata Barau ya kai ziyarar jaje ga iyalan ‘yan wasan da suka rasu, ya bayar da gudunmuwar N22m

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I Jibrin, a...

Hawan sallah : Sarki Sanusi ya umarci hakimai su shigo cikin birnin Kano

Majalisar Masarautar Kano ta fitar da wata takarda mai...

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...