Gobara ta kashe uwa da ɗanta a Kano

Date:

 

A jiya Alhamis ne wani ibtila’i , ya faru a unguwar Gandun Albasa, a layin Bala Burodo a birnin Kano, inda wata uwa mai suna Maryam Nura mai shekaru 35 da ɗanta ɗan shekara uku suka mutu sakamakon gobara da ta ƙone ginin da suke zaune a ciki. .

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Saminu Abdullahi ya fitar a yau Juma’a a Kano.

Abdullahi ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a jiya Da daddare.

“Mun samu kiran gaggawa da misalin karfe 2:07 na safe daga wani Ibrahim Ashiru kuma nan take muka aika da tawagarmu zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 2:11 na safe,” inji shi.

Ya ce “Ginin, gida ne mai dakuna biyar mai tsayin taku 75ft da 75ft, kuma gobarar ta rushe shi gaba daya.”

Daily Nigeria ta rawaito Abdullahi ya ce, an ceto wadanda lamarin ya rutsa da su ne a sume kuma aka mika su ga Insfekta Shehu Lawan na ofishin ‘yan sanda na Ƙwalli, inda suka garzaya da su asibitin kwararru na Murtala Muhammad, inda a nan ne kuma likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...