Yanzu-Yanzu: Salihu Tanko Yakasai ya fice daga jam’iyyar APC

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Tsohon mashawarci ga Gwamnan jihar kano akan harkokin yada labarai Salihu Tanko Yakasai ya ce ya fice jam’iyyar APC Saboda Rashin sauke alkawuran da ta yiwa al’ummar Kasar nan.

Kadaura24 ta rawaito Salihu Tanko Yakasai ya bayyana hakan ne yayin taron Manema labarai a nan kano.

Salihu Tanko Wanda ake yiwa lakabi da Dawisu yace Jam’iyyar APC ta gaza sauke mafi yawa daga cikin nauye-nauyen data daukarwa yan Nigeria, dama abubun da ya kamata ace gwamnati ta yiwa al’ummar ta.

Da ni Kai tallan jam’iyyar APC a dukkanin mafi yawa daga cikin jihohin Nigeria , Kuma mun yiwa al’ummar kasar nan alkawura Amma ni da kaina na gamsu da Cewa jam’iyyar ta gaza dauke alkawuran data yiwa yan kasa”. Inji Salihu Tanko Yakasai

Salihu Yakasai Wanda Gwamnatin kano ta dauke daga mukaminsa Saboda irin kalaman da yake yiwa Gwamnatin tarayya na fadin Rashin tabukawa Yan Kasa komai yace ya Dade yana fadawa gwamnatoci gaskiya tun lokaci da PDP ta ke Kan mulki.

Saboda irin Matsalolin da Yan Ƙasar nan suke cikin na Rashin tsaro, rashin baiwa yan kasa kyakykyawar rayuwa ,Sanya Yan kasa cikin Mawuyacin halin dama Wasu Matsalolin hakan tasa na fice daga jam’iyyar APC a wannan rana”.inji Salihu Yakasai

Tanko Yakasai yace nan gaba kadan Zai baiyana Inda Zai Koma domin cigaba da gwagwarmayar Siyasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...