Da dumi-dumi: El-Rufa’i ya sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a wasu kananan Hukumomin Jihar

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru
 Biyo bayan shawarwarin da hukumomin tsaro suka bayar, gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a kananan hukumomin Jema’a da Kaura Kuma tuni dokar ta fara aiki.
 Kadaura24 ta rawaito hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Samuel Aruwan.
 Sanarwar ta ce an dauki Wannan mataki domin taimakawa jami’an tsaro don daidaita al’amura da kuma dawo da doka da oda a yankunan.
 Ta kuma bayyana cewa, hukumomin tsaro na da cikakken ikon aiwatar da dokar ta-bacin, inda gwamnati ta yi kira ga daukacin mazauna kananan hukumomin Jema’a da Kaura da su baiwa jami’an tsaro hadin don dawo da zaman lafiya da bin doka da oda cikin gaggawa.
 Sai dai sanarwar ta ce gwamnati ta yi Allah-wadai da tashe-tashen hankula da kuma duk wasu ayyukan ta’addanci da suka afku a yankin, domin za a fitar da karin bayani nan gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...