Matar wanda a ke zargi da kashe Hanifa ta bada shaida a kansa a kotu

Date:

 

A jiya Alhamis ne Jamila Sani, matar Abdulmalik Tanko, wanda a ke zargi da yin garkuwa da kuma kashe Hanifa Abubakar, ƴar shekara 5 a Jihar Kano, ta bada shaida a kan mijinta.

Tun a zaman kotun na jiha ne lauyan gwamnati, Musa A. Lawal ya gabatar da shaidu guda uku bayan da a zaman kotun na baya Tanko ya nisanta duk tuhume-tuhumen da a ke masa.

Shaidun sun haɗa jami’an ƴan sandan farin kaya, DSS biyu sai kuma ɗan sanda guda daya, wanda shi ne ma wanda ya binciki laifin.

Da a ke mata tambayoyi a zaman kotun na jiya, matar Tanko ta tabbatar da cewa ya kawo Hanifa gidan, inda ba ta fi tsawon kwanaki shida ba.

A cewar matar, da ta tambayi Tanko ko ƴar waye sai ya ce ai ƴar malamar da ke aiki a makarantar sa ne, inda ya ce mahaifiyarta ta samu aiki a Saudi Arebiya shi ne ta tafi Abuja domin cike wasu takardu.

Matar Tanko ɗin ta ƙara da cewa da wasa da wasa sai da Hanifa ta kwana shida a gidan su, sannan da daddare wajen ƙarfe 11 na dare ya ɗauke ta da ga gidan.

Da a ka nuna mata hoton Hanifa, matar Tanko ta tabbatar da cewa ita ce yarinyar da mijin nata ya kawo har ta yi kwanaki 6, har ma ta saba da ƴaƴan ta a gidan.

“Ban san cewa Hanifa ta mutu ba sai da jami’an DSS su ka zo gidan mu, sannan na san halin da a ke ciki,” in ji matar Tanko.

Kadaura24 ta rawaito cewa kawo yanzu dai, an gabatar da shaidu guda takwas a kotun.

Alƙalin kotun, Usman Na-abba, ya umarci a maida waɗanda a ke zargi gidan yari har sai ranar 9 da 10 ga watan Maris za a ci gaba da shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...