Mahaifiyar Limamin Masallacin Al-Furqan, Dakta Bashir Aliyu ta rasu

Date:

 

Mahaifiyar fitaccen Malamin addinin musuluncin nan na Jihar Kano, Dakta Bashir Aliyu Umar ta rasu.

Marigayiyar, mai suna Hajiya Khadija Aliyu Harazumi ta rasu da safiyar yau Talata a gidanta da ke Gwale Gudundi bayan ta yi rashin lafiya.

Hajiya Kahdija daya ce daga cikin matan Dan Amar Kano Alhaji Aliyu Harazumi Umar.

Ta rasu ta bar ƴaƴa da jikoki da dama.

Daga ciki akwai babban limamin masallacin juma’a na Al-Furqan da ke unguwar Nasarawa a birnin Kano Dr Bashir Aliyu Umar

Haka kuma za a yi jana’izarta a Kofar Kudu da ke gidan Sarkin Kano da misalin ƙarfe 3 na yamma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...