Ba a yiwa Buhari adalci akan Sanya hannu a dokar zabe – Garba Shehu

Date:

Fadar Shugaban Najeriya ta ce babu adalci idan aka zargi cewa shugaba Muhamamdu Buhari na jan kafa wajen sanya hannu a kan kudirin dokar zaɓe ta 2022.

Hakan na zuwa ne bayan ƙungiyoyin fararen hula da wasu masu ruwa da tsaki sun zargi shugaban da jan ƙafa wajen sa hannu a kan dokar duk da ɗumbin muhimmancinta.

Mai magana da yawun Shugaban ƙasar, Mallam Garba Shehu ya ce masu waɗannan zarge-zarge ba su yi wa shugaban adalci ba.

Sannan ya sake sake jadada cewa a ranar Juma’a 26 ga watan Fabarairu shugaba Buhari zai sa hannu kan ƙudurin dokar zaɓen da ake ce-ce-ku-ce a kanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...