Majalisar Dokokin Zamfara ta tantance Hassan Nasiha a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar

Date:

Daga Kamal Yahaya Bello

Awanni kaɗan bayan tsige Mahdi Aliyu Gusau, Majalisar Dokoki ta Jihar Zamfara ta tantance Sanata Hassan Nasiha a matsayin sabon Mataimakin Gwamna.

Nasiha shine Sanata mai ci da ke wakailtar Zamfara ta tsakiya a Majalisar Dattijai.

Ƴan majalisar sun tabbatar da Nasiha a matsayin sabon Mataimakin Gwamna a wata ƙuri’a ta bai-ɗaya.

Gwamnan Jihar, Bello Matawalle, a wata wasiƙa danya rubuta wa Sakataren Gwamnati, Kabiru Balarabe sannan Kakakin Majalisar, Nasiru Magarya ya karanta a zaman majalisar na yau Laraba, ya miƙa sunan Nasiha a matsayin sabon Mataimakin Gwamna bayan cire Mahdi Aliyu.

Sai Shugaban Masu Rinjaye, Faruku Dosara ya miƙa ƙudurin tabbatar da Nasiha, wanda dukka mambobin su ka amince.

Kakakin Majalisar ya baiyana cewa naɗin sabon Mataimakin Gwamnan ya yi daidai da tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin Ƙasa na 1999.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...