Ganduje ya samar da dakunan karatu a k/h 44 ne don cusawa dalibai dabi’ar karatu – Hafsat Ganduje

Date:

Daga Maryam adamu Mustapha
Gwamnatin jihar kano ta bayyana aniyarta na cigaba da bunkasa dakunan karatu wato library dake Jihar nan, domin bunkasa fannin ilimi tare da bukatar daliban dasu kasance masu gudanar da bincike da karatuttuka domin cigaban karatunsu
Kadaura24 ta rawaito Maidakin Gwamnan Jihar kano farfesa Hafsat Abdullahi Ganduje ce ta bayyana hakan yayin bada shaidar kammala daukar horo na ilimin na’ura mai kwakwalwa a fannoni daban-daban na mata da maza kimanin su 131 Wanda aka gudanar a dakin karatu dake jihar nan.
Mai dakin gwamnan tace hakanne ma yasa gwamnatin jiharkano ta Samar da dakunan karatu a kananan hukumomin jihar 44 don bunkasa Karatun dalibai da Kuma cusa musu dabi’ar yin Karatu.
Farfesa Hafsat Ganduje ta kara da cewa rashin maida hankali wajen karatun dalibai shi ke Kawo musu koma baya a sha’anin Karatun, a don haka ta bukaci iyaye dasu tashi tsaye wajen ganin ‘ya’yansu sun sami ilimi mai nagarta. Ta kuma  bukaci daliban Jihar Kano da su kasance masu nacin karatu musamman a dakunan karatun da ake dasu domin bunkasa harkokin ilimi aj ihar dama kasa baki daya .
Farfesa Hafsat Ganduje ta bukaci daliban da suka sami horon da suyi amfani dashi yadda ya dace duba da cewa a yanzu haka an zamanantar da harkar karatu ta fannin na’ura mai kwakwalwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...