Waɗanda Suka Kashe Hanifa Abubakar sun sami lauyan da zai kare su

Date:

Babban lauyan gwamnati kuma Kwamishinan shari’a na jihar Kano, Barrister Musa Abdullahi Lawan,ya bayyana cewa hukumar bayar da tallafin shari’a ta Najeriya (Legal Aid Council of Nigeria) ta nuna aniyarta ta samar da lauyoyin da za su wakilci mutanen da ake zargi da sacewa da kuma kashe yarinyar nan Hanifa Abubakar.

Jaridar DailyTrust ta ruwaito cewa, kwamishinan ya fada mata a ranar Alhamis din nan cewa, matakin ya biyo bayan umarnin da mai shari’a Usman Na’abba na babbar kotun Kano ya yi ne a ranar 5 ga watan nan na Fabrairu cewa gwamnatin jihar ta sama wa babban wanda ake zargin da sauran mutum biyu lauya, kamar yadda suka bukaci lauya ya tsaya musu a shari’ar, saboda ba su da shi.

Babban lauyan na gwamnatin Kano ya ce, a bisa doka duk mutumin da yake fuskantar shari’ar zargin kisan kai, ana bukatar ya samu lauya mai wakiltarsa, idan kuma ba shi da lauyan ba kuma shi da halin dauka, tsarin mulki Najeriya ya sa dole jiha ta sama masa.

Atoni Janar din ya kara bayani da cewa hukumar bayar da tallafin shari’ar ta Najeriya hukuma ce ta tarayya wadda aka kafa ta domin taimaka wa duk wani dan kasar da ba shi da lauya a shari’ar da ake masa mai hukuncin kisa, kyauta.

An dakatar da shari’ar Abdulmalik Tanko da mutum biyu da ake zargi da sacewa da kuma kashe Hanifa saboda ba su da lauyan da zai kare su.

Daman alkalin da ke shari’ar ya dage zama har zuwa ranar 14 ga watan nan na Fabrairu, bayan da ya gabatar da umarnin a sama musu lauya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...