Bunkasa Noma: Shirin KSADP na samun gagarumar nasara a Kano

Date:

Daga Aminu Indabawa

Gagarumin shirin nan na bunkasa noma da kiwo na Jihar Kano KSADP shirin da gwamnatin Jihar Kano karkashin Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya samu tallafin kudi daga bankin addinin musulunci dake Jidda da wasu hukumomi wanda hukumar bunkasa aikin gona ta KNARDA ta ware wani bangare domin lura da shirin don bunkasa shi.

A daidai lokacin da shirin ya shiga shekara ta biyu cibiyar Sassakawa Africa Association (SAA) tayi taron masu ruwa da tsaki a shirin da suke hada da ICRASAT, IITA kamfanunonin saye da sayarwar kayan amfanin gona da bunkuna domin jin rahotannin irin abubuwan da suke gaba a shirin.
Taron ya samu halartar Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna wanda shine shugaban kwamitin, Wanda Gawuna ya samu wakilcin babban sakatare a ma’aikatar gona ta Jihar Alhaji Balarabe Karaye ya Wakilta ya nuna jin dadi da gamsuwar sa akan yadda shirin yake gudana.
 Shugaban Sassakawa na kasa Prof. Sani Miko ya yi tsokaci akan yadda cibiyar tasa ta himmatu wajen ganin ta sauke nauyin da ake dora mata.
 Shi ma shugaban hukumar KNARDA Dr. Junaidu Yakubu Muhammad da shugaban gudanar da shirin na jiha Mal. Ibrahim Garba sun yaba da yadda suka tabbatar da gaskiya da Sassakawa keyi wajen aiwatar da shirin na KSADP.
Mahalarta taro musamman masu ruwa da tsaki sun tattauna inda a qarshe aka gamsu anyi nasara kuma za’a ribanya nasarar anan gaba.
 Daga bisani aka raba babura guda (29) ga malaman gonar da ake wannan aiki dasu qari akan guda (90) da aka raba a shekarar data gabata, inda shugaban shirin na Jiha Mal. Ibrahim Garba yayi albishirin sahalewar cibiyar ta Sassakawa siyen guda (100) nan gaba duba da irin kokarin da sukayi na siyan ingatattun babura.
Suma wadanda suka rabauta da wadannan babura sun nuna jin dadin su, tare da aniyar rubanya kokarinsu wajen gudanar da ayyukan dake gabansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...