Aisha Buhari ta ziyarci Kano don yin ta’aziyyar Hanifa Abubakar

Date:

Daga Maryam adamu Mustapha
Uwar gidan Shugaban Kasa Aisha Buhari ta ja hankalin gwamnatin Kano da ta dauki matakan kariya ga Kananan Yara don gudun kara afkuwar abin da ya faru da yarinyar nan Haneefa Abubakar da malaminta ya yiwa kisan gilla a nan Kano.
Uwar gidan shugaban kasa ta bayyana hakan ne lokacin da ta zo Gidan Gwamnatin Jihar Kano don yiwa Gwamnati da  Iyayen Hanifa Abubakar ta’aziyyar  Rasuwarsu .
Aisha Buhari ta yabawa Gwamnatin Jihar Kano bisa matakan data dauka tun faruwar lamarin, Sannan  ta ce saurin yanke hukunci ga Waɗanda aka Samu da Wannan laifi zai kwantar da hankalin iyaye musamman mata.
Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya jaddadawa al’ummar Kano cewa gwamnatin Kano ba za ta kara ko minti guda ba wajen sanya hannu, Idan Kotu ta yanke hukuncin kisa akan Waɗanda ake Zargi.
Uwar gidan Shugaban Kasar ta Ziyarci Fadar Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero domin yi Masa ta’aziyyar rashe-rashen da akai a Kano a yan watannin baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NAHCON ta sanar da ranar da za a fara jigilar Maniyatan Nigeria zuwa kasar Saudiyya

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar kula da aikin hajji ta...

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma’aiki ya fito a jihar Kano

    Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani...

ƴan siyasa ne su ka kashe Arewacin Nigeria — Inji Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ‘yan...

Shugaban Karamar hukumar Bagwai ya kaddamar da aikn gada ta sama da Naira Miliyan 160

Daga Shu'aibu Sani Bagwai   Karamar hukumar Bagwai a jihar Kano...