2023: Sheikh Ibrahim Khalil da Dr Dukawa sun koma jam’iyyar ADC

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

Bayan bayyana ficewarsa daga jam’iyya mai mulki ta APC a karshen shekarar da ta gabata ta 2021, shugaban majalisar malamai ta jihar Kano, Sheik Ibrahim Khalil, ya shiga jam’iyyar ADC, wanda kuma nan gaba kadan za’a shirya taron karbarsa cikin jam’iyyar.

Bayanin komawa jam’iyyar ADC da malamin yayi, na kunshe cikin wani sako da shugaban jam’iyyar na jihar Kano, Shu’aibu Ungoggo, ya gabatar ga manema labarai a yau juma’a.

Cikin bayanin nasa, Shu’aibu Ungoggo, yace malamin ya shigo jam’iyyar tasu ta ADC ne tare da Dakta Sa’idu Ahmad Dukawa na jami’ar Bayero, da kuma wasu malaman jami’a guda takwas da suka rufa masa baya, a kokarinsu na ganin cewa an ceto jihar Kano daga halin da ta ke ciki, a cewarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...