Gwamnatin Najeriya ta gano masu daukar nauyin Boko Haram 96

Date:

 

Hukumar da ke tattara bayanan sirri kan kudade ta bankado masu samar da kudi dan ta’addamci 96 har da masu alaka da kamfanonin hada-hadar kudi 424.

Ministan yada lanarai da al’adu na Najeriya Lai Mohammed ne ya bayyana hakan ne a yau, yayin wani bayani da ya yi kan yaki da cin hanci da gwamnatin shugaba Buhari ke yi.

Ya kara da cewa an gano kamfanoni 123 da kamfanonin 33 na masu musayar kudi da ke da alaka da ‘yan ta’adda a Najeriya.

Ya ce, “A bangarenta, a sharhin da ta yi kan kudade na 2020-2021, ta bayyana masu hada-hadar kudade 96 da ke da alaka da ‘yan ta’adda a Najeriya, akwai kuma wasu 424 da ke samar da kudade domin ta’addanci da suka hadar da kamfanoni 123, da kuma na masu musayar kudi 33, bugu da kari an gano wasu 26 da ake zargi da ta’addanci da wasu 7 da ake hada kai da su kan harkokin ta’addanci. Wannan bayani ya kai ga kama 45 da ake zargi wadanda kwanan nan za a gabatar da su a gaban kotu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...