Hadarin Mota: Kwamishinan muhalli na Kano ya kai daukin gaggawa, ya ceci Waɗanda suka jikkata

Date:

Daga Adam Bichi

Wani mummunan hadarin mota ya afku a kan titin Aminu Kano, da ke unguwar Goron Dutse, yayin da wani Driban mota kirar Toyota Corolla ke yunkurin wuce wata motar kirar Peugeout 406.

KADAURA24 ta rawaito waddanda suka gane wa idonsu yadda hadarin ya afku, sun ce hadarin ya faru ne sakamakon gudun wuce-sa’a da direban Corollar yake yi.

Afkuwar hadarin ke da wuya, sai tawagar Kwamishinan Ma’aikatar Muhalli ta Jihar Kano, Dakta Kabiru Ibrahim Getso ta iso wurin. Nan take Kwamishinan, wanda yake kuma kwararren likita ne, ya nuna tausayawarsa, ya ba da gudumawar gaggawa, kuma ya umarci a dauki wadanda suka ji rauni kafin a kai su zuwa asibiti.

Sakon taya Murnar Samun shugabancin jam’iyyar SDP a Jihar Kano

Cikin Sanarwar da jami’in hurda da jama’a na Ma’aikatar Muhalli ta Jihar Kano  Sunusi A. K/Naisa ya aikowa Kadaura24 yace, Dakta Getso ya yi addu’ar samun sauki ga wandanda suka ji raunuka. Sannan ya gargadi direbobi da su guji tukin ganganci da gudun-wuce-sa’a.

Kwamishina Dakta Getso ya ba da gudunmawar ne lokacin da yake kewayen duba aikin tsaftar Muhalli na karshen wata. Yayin zagayen, Dakta Getso yana tare da kwamitin kar ta kwana na Tsaftar Muhalli na jiha wanda ya kunshi jami’an Ma’aikatar Muhalli da jami’an tsaro da ‘yan jarida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...