Kano pillars a karon farko ta samu maki uku a waje a gasar 2021/2022 NPFL.

Date:

 

Zaharadeen saleh

A karon farko a kakar wasa ta bana kungiyar kwallon kafa ta kano pillars ta samu maki uku a waje bayan data samu nasarar doke kungiyar kwallon kafa Heartland dake garin Owerri jihar Imo, har gida daci daya babu ko daya a zagayen wasa mako na tara da aka shiga a cigaba da gasar cin kofin kwallon kafa ajin firimiya ta Nigeria, ta kakar wasa ta shekara ta 2021/2022.

Dan wasan kungiyar kano pillars mai suna Mark Daniel daya shigwo wasan a mintina 87 shine ya samu nasarar jefa kwallo daya tilo aragar Heartland, a mintina 90 wanda ya bawa kano pillars nasarar samu maki uku a wasan da suka fafata a asabar din nan.

Yanzu haka bisa nasarar da kano pillars ta samu ta dawo matsayi na shida da maki 13 a gasar firimiya Nigeria.

A sauran wasanin da aka fafata a asabar din nan kungiyar kwallon kafa ta Enyimba International dake garin Aba jihar Abia , ta samu nasarar doke kungiyar Katsina united daci biyu da daya, itama kungiyar Sunshine Stars dake garin Akure jihar Ondo ta lilisa kungiyar Lobi Stars dake garin Makurdi daci uku da nema.

A yammancin ranar Lahadin ce idan Allah yakaimu za’a fafata ragowar wasanin guda bakwai na zagayen wasa mako na tara da aka shiga.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zaizayar kasa: Gwamna Abba gida-gida ya raba diyyar Naira Miliyan 600 A Kano

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Dalilin da ya hana Sarki Aminu Ado Bayero zuwa gidan yari na goron dutse a yau alhamis

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Rahotanni sun tabbatar da cewa Sarkin...

Matakai 3 da gwamnatin Kano ta dauka kan kafafen yada labarai a jihar

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano ta ce a...

Yadda manoma a Kano suka zargi jami’an Civil defense da karbar kudade a wajensu

Daga Umar Ibrahim kyarana   Manoman dajin dansoshiya dake karamar hukumar...